Khalifa Muhammad Sanusi II ya umarci yan Kaduna da su Goyi bayan Uba Sani a zaɓen 2023

Advertisements

Tsohon Sarkin Kano kuma jagoran Ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya, Khalifa Muhammad Sanusi II, ya umarci mabiyansa su zabi Uba Sani ya zama gwamnan Kaduna.
A wurin taron shekara-shekara a Kaduna, Sheikh Tijani Inyass yace Khalifa ya umarci su mara wa APC baya a Kaduna, ya kuma gaya musu wanda zasu zaɓa a Kano.
Kaduna – Tsohon Sarkin Kano kuma jagoran Ɗariƙar Tijjaniyya a Najeriya, Khalipha Muhammad Sanusi II, ya nuna goyon bayansa ga ɗan takarar gwamnan Kaduna a inuwar jam’iyyar APC. 
Sheikh Tijjani Sani Auwal Inyass, ɗaya daga cikin masu faɗa aji a Ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya ne ya bayyana haka a taron shekara na farko na ƙungiyar Tijanniya Grassroots Mobilisation and Empowerment (TIGMIEN)
Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like