BABBAR NASARA: Sojoji Nijeriya sun ragargaji yan Boko Haram a Borno

Advertisements

Rundunar Sojin Najeriya ta ce, Sojoji sun kashe ‘yan ta’addar Boko Haram a Borno, sun kwato manyan bindigogi da makamai

Advertisements

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarun Operation Hadin Kai sun kashe wasu ‘yan kungiyar ta’adda ta Boko Haram/Daular Islama a yammacin Afirka.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka fitar a shafin Twitter na rundunar sojojin Najeriya a ranar Juma’a.
A cewar rundunar, an kashe ‘yan ta’addan ne bayan wani samame da suka kai a kusa da hanyar Wajiroko zuwa Damboa a jihar Borno.
Kayayyakin da aka kwato daga hannun ‘yan ta’addan sun hada da manyan motoci da makamai da alburusai.
Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like