Yan sanda sun kama matashin da ya kashe kishiyar Mahaifiyarsa da ƴarta a Kano

Advertisements

Wani matashi ɗan shekara 20, mai suna Gaddafi Sagir, ya kashe kishiyar mahaifiyarsa mai suna Rabi da kuma yar ta, Munawwara a jihar Kano.

Yana da kyau ka duba wannan👉 https://bit.ly/3ruFOdf

Lamarin ya faru ne a jiya Asabar da misalin ƙarfe 10 ma dare a unguwar Fadama da ke Rijiyar Zaki a jihar Kano.

Duba wannan 👉 https://bit.ly/3OerbEx

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa matashin na zargin marigayiya Rabi da yin sanadiyyar rabuwa da mahaifinsa, shi ne ya buga mata ƙarfe a wuya da goshi, nan take ta faɗi ta rasu da tsohon ciki a jikin ta

Advertisements

Ka karanta wannan kuwa 👉 https://bit.ly/3OjYt59

Rundunar ƴan sanda a Kano, ta bakin kakakin ta, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka rundunar ta kama wanda ake zargin, inda ya ce a yayin binciken farko, ya amsa cewa shi ne ya kashe mamatan.

Ƙarin bayani na nan tafe…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like