Zaɓen 2023 Hukumar shige da fice ta Ƙasa ta kama wasu ‘yan Ƙasar waje da Katin Zaɓen Nijeriya

Advertisements

An kama wasu ‘yan kasar waje mazauna Najeriya da suka mallaki katin zabe yayin da zabe ke karatowa An kwato katukan zabe 106 a jihar Kwara.
 Hukumar shige da fice ta yi karin haske game da halin da ake ciki Saura kwanakin kadan a yi babban zaben 2023, an gargadi ‘yan kasar waje su guji yin zaben a Najeriya.
Ilorin, jihar Kwara – Hukumar kula shige da fice ta Najeriya (NIS) ta kama katukan zabe na PVC guda 106 a hannun wasu ‘yan kasar waje a jihar Kwara, TheCable ta ruwaito.
 Aminu Shamsuddin, kwamtulan NIS a jihar ne ya bayyana hakan a ranar Litinin 6 Faburairu, 2023, inda yace an kama ‘yan kasar wajen ne a yayin sintirin da jami’an hukumar ke yi a birnin Ilorin na jihar.
A lokacin wani shirin wayar da kan, ‘yan kasar waje sun tsorata da jin cewa duk wanda aka kama shi ya kusanci zaben Najeriya zai sha dauri, a maida shi kasarsu kana a sanya shi a bakin jadawali. 
“Wasu daga cikin ‘yan kasar wajen da ke da katin zaben Najeriya da kansu suka ajiye katukan kuma suka koma kasashensu, za su dawo bayan kammala zaben. 
Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like