Advertisements
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙammadar da aikin haƙar rijiyar man fetu a ƙaramar hukumar Obi a jihar Nasarawa da ke arewa ta tsakiyar ƙasar.
Ƙaddamar da aikin tona rijiyar zai sa kamfanin mai na ƙasar NNPC Ltd, ta fara tono man fetur daga jihar.
A cikin watan Nuwamban bara ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe a yankin arewa maso gabashin ƙasar.
Yawancin man da ƙasar ke da shi dai tana haƙoshi ne daga yankin Niger Delta a kudu maso kudancin ƙasar.
Najeriya dai ta dogara ne kan man fetur da take fitarwa a matsayin hanayr samun kuɗin shiga, duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnatocin ƙasar ke yi na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga ga ƙasar.